Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/59

الدخان

Ad-Dukhan

Duhân

Makkiyya·Ayoyi 59

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

44:1
Juz'i 25
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

حمٓ﴿١﴾

Ḥ. M̃.

—
44:2
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

وَٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ﴿٢﴾

Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.

—
44:3
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

إِنَّآ أَنزَلْنَـٰهُ فِى لَيْلَةٍ مُّبَـٰرَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ﴿٣﴾

Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.

—
44:4
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ﴿٤﴾

A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.

—
44:5
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

أَمْرًا مِّنْ عِندِنَآ ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ﴿٥﴾

Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.

—
44:6
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

رَحْمَةً مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلْعَلِيمُ﴿٦﴾

Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.

—
44:7
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

رَبِّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ﴿٧﴾

(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).

—
44:8
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْىِۦ وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ﴿٨﴾

Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.

—
44:9
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

بَلْ هُمْ فِى شَكٍّ يَلْعَبُونَ﴿٩﴾

A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.

—
44:10
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

فَٱرْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِى ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٍ مُّبِينٍ﴿١٠﴾

Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.

—
44:11
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

يَغْشَى ٱلنَّاسَ ۖ هَـٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ﴿١١﴾

Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.

—
44:12
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

رَّبَّنَا ٱكْشِفْ عَنَّا ٱلْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ﴿١٢﴾

Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.

—
44:13
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَآءَهُمْ رَسُولٌ مُّبِينٌ﴿١٣﴾

Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?

—
44:14
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

ثُمَّ تَوَلَّوْا۟ عَنْهُ وَقَالُوا۟ مُعَلَّمٌ مَّجْنُونٌ﴿١٤﴾

Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."

—
44:15
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

إِنَّا كَاشِفُوا۟ ٱلْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَآئِدُونَ﴿١٥﴾

Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).

—
44:16
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

يَوْمَ نَبْطِشُ ٱلْبَطْشَةَ ٱلْكُبْرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ﴿١٦﴾

Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.

—
44:17
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

۞ وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَآءَهُمْ رَسُولٌ كَرِيمٌ﴿١٧﴾

Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.

—
44:18
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 496

أَنْ أَدُّوٓا۟ إِلَىَّ عِبَادَ ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ﴿١٨﴾

(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."

—
44:19
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَأَن لَّا تَعْلُوا۟ عَلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّىٓ ءَاتِيكُم بِسُلْطَـٰنٍ مُّبِينٍ﴿١٩﴾

"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."

—
44:20
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَإِنِّى عُذْتُ بِرَبِّى وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ﴿٢٠﴾

"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."

—
44:21
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا۟ لِى فَٱعْتَزِلُونِ﴿٢١﴾

"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."

—
44:22
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوْمٌ مُّجْرِمُونَ﴿٢٢﴾

Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.

—
44:23
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

فَأَسْرِ بِعِبَادِى لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ﴿٢٣﴾

(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"

—
44:24
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَٱتْرُكِ ٱلْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌ مُّغْرَقُونَ﴿٢٤﴾

"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."

—
44:25
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

كَمْ تَرَكُوا۟ مِن جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ﴿٢٥﴾

Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.

—
44:26
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَزُرُوعٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ﴿٢٦﴾

Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.

—
44:27
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَنَعْمَةٍ كَانُوا۟ فِيهَا فَـٰكِهِينَ﴿٢٧﴾

Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.

—
44:28
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَـٰهَا قَوْمًا ءَاخَرِينَ﴿٢٨﴾

Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.

—
44:29
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ ٱلسَّمَآءُ وَٱلْأَرْضُ وَمَا كَانُوا۟ مُنظَرِينَ﴿٢٩﴾

Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.

—
44:30
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ مِنَ ٱلْعَذَابِ ٱلْمُهِينِ﴿٣٠﴾

Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.

—
44:31
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَالِيًا مِّنَ ٱلْمُسْرِفِينَ﴿٣١﴾

Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.

—
44:32
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَلَقَدِ ٱخْتَرْنَـٰهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿٣٢﴾

Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.

—
44:33
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَءَاتَيْنَـٰهُم مِّنَ ٱلْـَٔايَـٰتِ مَا فِيهِ بَلَـٰٓؤٌا۟ مُّبِينٌ﴿٣٣﴾

Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna

—
44:34
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَيَقُولُونَ﴿٣٤﴾

Lalle waɗannan mutãne, haƙĩka, sunã cẽwa,

—
44:35
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

إِنْ هِىَ إِلَّا مَوْتَتُنَا ٱلْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ﴿٣٥﴾

"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."

—
44:36
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

فَأْتُوا۟ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمْ صَـٰدِقِينَ﴿٣٦﴾

"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."

—
44:37
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍ وَٱلَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَـٰهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ مُجْرِمِينَ﴿٣٧﴾

shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.

—
44:38
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

وَمَا خَلَقْنَا ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَـٰعِبِينَ﴿٣٨﴾

Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.

—
44:39
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 497

مَا خَلَقْنَـٰهُمَآ إِلَّا بِٱلْحَقِّ وَلَـٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ﴿٣٩﴾

Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.

—
44:40
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ مِيقَـٰتُهُمْ أَجْمَعِينَ﴿٤٠﴾

Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.

—
44:41
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

يَوْمَ لَا يُغْنِى مَوْلًى عَن مَّوْلًى شَيْـًٔا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ﴿٤١﴾

Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.

—
44:42
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

إِلَّا مَن رَّحِمَ ٱللَّهُ ۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ﴿٤٢﴾

fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

—
44:43
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

إِنَّ شَجَرَتَ ٱلزَّقُّومِ﴿٤٣﴾

Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),

—
44:44
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

طَعَامُ ٱلْأَثِيمِ﴿٤٤﴾

Ita ce abincin mai laifi.

—
44:45
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

كَٱلْمُهْلِ يَغْلِى فِى ٱلْبُطُونِ﴿٤٥﴾

Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.

—
44:46
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

كَغَلْىِ ٱلْحَمِيمِ﴿٤٦﴾

Kamar tafasar ruwan zãfi.

—
44:47
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

خُذُوهُ فَٱعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلْجَحِيمِ﴿٤٧﴾

(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."

—
44:48
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

ثُمَّ صُبُّوا۟ فَوْقَ رَأْسِهِۦ مِنْ عَذَابِ ٱلْحَمِيمِ﴿٤٨﴾

"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."

—
44:49
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ ٱلْعَزِيزُ ٱلْكَرِيمُ﴿٤٩﴾

(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"

—
44:50
Juz'i 25 · Hizbi 50 · Shafi 498

إِنَّ هَـٰذَا مَا كُنتُم بِهِۦ تَمْتَرُونَ﴿٥٠﴾

"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."

—
Aya Da Ta GabataAz-ZukhrufAya Mai ZuwaAl-Jathiyah