Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/135

طه

Taha

Tâ-Hâ

Makkiyya·Ayoyi 135

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

20:1
Juz'i 16
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

طه﴿١﴾

¦.H.

—
20:2
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

مَآ أَنزَلْنَا عَلَيْكَ ٱلْقُرْءَانَ لِتَشْقَىٰٓ﴿٢﴾

Ba Mu saukar da Alƙur'ãni a gare ka dõmin ka wahala ba.

—
20:3
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

إِلَّا تَذْكِرَةً لِّمَن يَخْشَىٰ﴿٣﴾

Fãce dõmin tunãtarwa ga wanda ke tsõron Allah.

—
20:4
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

تَنزِيلًا مِّمَّنْ خَلَقَ ٱلْأَرْضَ وَٱلسَّمَـٰوَٰتِ ٱلْعُلَى﴿٤﴾

(An saukar da shi) saukarwa daga wanda Ya halitta ƙasa da sammai maɗaukaka.

—
20:5
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

ٱلرَّحْمَـٰنُ عَلَى ٱلْعَرْشِ ٱسْتَوَىٰ﴿٥﴾

Mai rahama, Ya daidaita a kan Al'arshi.

—
20:6
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

لَهُۥ مَا فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَمَا فِى ٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَمَا تَحْتَ ٱلثَّرَىٰ﴿٦﴾

Abin da yake a cikin sammai nãSa ne, da abin da yake a cikin ƙasa da abin da yake a tsakãninsu da abin da ke ƙarƙashin turɓãya.

—
20:7
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

وَإِن تَجْهَرْ بِٱلْقَوْلِ فَإِنَّهُۥ يَعْلَمُ ٱلسِّرَّ وَأَخْفَى﴿٧﴾

Kuma idan ka bayyana da magana, to, lalle Shi, Yanã sanin asĩri da mafi bõyuwa.

—
20:8
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

ٱللَّهُ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا هُوَ ۖ لَهُ ٱلْأَسْمَآءُ ٱلْحُسْنَىٰ﴿٨﴾

Allah bãbu abin bautãwa fãce Shi. Yanã da sunãye mafiya kyau.

—
20:9
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

وَهَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ﴿٩﴾

Kuma shin, lãbarin Mũsã yãje maka?

—
20:10
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

إِذْ رَءَا نَارًا فَقَالَ لِأَهْلِهِ ٱمْكُثُوٓا۟ إِنِّىٓ ءَانَسْتُ نَارًا لَّعَلِّىٓ ءَاتِيكُم مِّنْهَا بِقَبَسٍ أَوْ أَجِدُ عَلَى ٱلنَّارِ هُدًى﴿١٠﴾

A lõkacin da ya ga wata wuta, sai ya ce wa iyãlinsa, "Ku dãkata. Lalle ne nĩ, na tsinkãyi wata wuta tsammãnĩna in zo mukuda makãmashi daga gare ta, kõ kuwa in sãmi wata shiriya a kan wutar."

—
20:11
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِىَ يَـٰمُوسَىٰٓ﴿١١﴾

Sa'an nan a lõkacin da ya je mata, aka kira shi, "Ya Mũsã!"

—
20:12
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 312

إِنِّىٓ أَنَا۠ رَبُّكَ فَٱخْلَعْ نَعْلَيْكَ ۖ إِنَّكَ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى﴿١٢﴾

"Lalle ne, Nĩ ne Ubangijnka, sai ka ɗẽbe takalmanka Lalle ne kanã a rãfin nan abin tsarkakẽwa, ¦uwa."

—
20:13
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَأَنَا ٱخْتَرْتُكَ فَٱسْتَمِعْ لِمَا يُوحَىٰٓ﴿١٣﴾

"Kuma Nĩ Nã zãɓe ka. Sai ka saurãra ga abin da ake yin wahayi."

—
20:14
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

إِنَّنِىٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعْبُدْنِى وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكْرِىٓ﴿١٤﴾

"Lalle, Nĩ Ni ne Allah. Bãbu abin bautawa fãce Ni. Sai ka bauta Mini, kuma ka tsayar da salla dõmin tuna Ni."

—
20:15
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخْفِيهَا لِتُجْزَىٰ كُلُّ نَفْسٍۭ بِمَا تَسْعَىٰ﴿١٥﴾

"Lalle ne Sa'a mai zuwa ce, lnã kusa da In ɓõye ta dõmin a sãka wa dukan rai da abin da yake aikatãwa."

—
20:16
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنْهَا مَن لَّا يُؤْمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرْدَىٰ﴿١٦﴾

"Sabõda haka, kada wanda bã ya yin ĩmãni da ita kumaya bi son zuciyarsa, ya taushe ka daga gare ta har ka halaka."

—
20:17
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَمَا تِلْكَ بِيَمِينِكَ يَـٰمُوسَىٰ﴿١٧﴾

"Kuma wãce ce waccan ga dãmanka yã Mũsa!"

—
20:18
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

قَالَ هِىَ عَصَاىَ أَتَوَكَّؤُا۟ عَلَيْهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِى وَلِىَ فِيهَا مَـَٔارِبُ أُخْرَىٰ﴿١٨﴾

Ya ce: "Ita sandãta ce, inã dõgara a kanta, kuma inã kakkaɓar ganye da ita a kan ƙananan bisãshẽna kuma inã da waɗansu bukãtõci na dabam a gare ta."

—
20:19
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

قَالَ أَلْقِهَا يَـٰمُوسَىٰ﴿١٩﴾

Ya ce: "Ka yi jĩfa da ĩta, yã Mũsã!"

—
20:20
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

فَأَلْقَىٰهَا فَإِذَا هِىَ حَيَّةٌ تَسْعَىٰ﴿٢٠﴾

Sai ya jẽfa ta. Sai gã ta dabbar macĩjiya, tanã tafiya da gaggãwa.

—
20:21
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

قَالَ خُذْهَا وَلَا تَخَفْ ۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا ٱلْأُولَىٰ﴿٢١﴾

Ya ce: "Ka kãma ta kuma kada ka ji tsõro. Za Mu mayar da ita ga hãlinta na farko."

—
20:22
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَٱضْمُمْ يَدَكَ إِلَىٰ جَنَاحِكَ تَخْرُجْ بَيْضَآءَ مِنْ غَيْرِ سُوٓءٍ ءَايَةً أُخْرَىٰ﴿٢٢﴾

"Kuma ka haɗa hannunka zuwa ga damtsenka, ya fita yanã fari, bãbu sõfane, wata ãyã ta dabam."

—
20:23
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

لِنُرِيَكَ مِنْ ءَايَـٰتِنَا ٱلْكُبْرَى﴿٢٣﴾

"Dõmin Mu nũna maka daga ãyõyinMu manya."

—
20:24
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ﴿٢٤﴾

"Ka tafi zuwa ga Fĩr'auna. Lalle shĩ ya ƙẽtare haddi (da girman kai)."

—
20:25
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

قَالَ رَبِّ ٱشْرَحْ لِى صَدْرِى﴿٢٥﴾

Ya ce: "Ya Ubangiji! Ka buɗa mini, ƙirjĩna.

—
20:26
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَيَسِّرْ لِىٓ أَمْرِى﴿٢٦﴾

"Kuma ka sauƙaƙe mini al'amarĩna."

—
20:27
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَٱحْلُلْ عُقْدَةً مِّن لِّسَانِى﴿٢٧﴾

"Kuma Ka warware mini wani ƙulli daga harshẽna."

—
20:28
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

يَفْقَهُوا۟ قَوْلِى﴿٢٨﴾

"Su fahimci maganãta."

—
20:29
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَٱجْعَل لِّى وَزِيرًا مِّنْ أَهْلِى﴿٢٩﴾

"Kuma Ka sanya mini wani mataimaki daga mutãnena."

—
20:30
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

هَـٰرُونَ أَخِى﴿٣٠﴾

"Hãrũna ɗan'uwana."

—
20:31
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

ٱشْدُدْ بِهِۦٓ أَزْرِى﴿٣١﴾

"Ka ƙarfafa halittata da shi."

—
20:32
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَأَشْرِكْهُ فِىٓ أَمْرِى﴿٣٢﴾

"Kuma Ka shigar da shi a cikin al'amarina."

—
20:33
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

كَىْ نُسَبِّحَكَ كَثِيرًا﴿٣٣﴾

"Dõmin mu tsarkake Ka da yawa."

—
20:34
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَنَذْكُرَكَ كَثِيرًا﴿٣٤﴾

"Kuma mu tuna Ka da yawa."

—
20:35
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

إِنَّكَ كُنتَ بِنَا بَصِيرًا﴿٣٥﴾

"Lalle Kai, Ka kasance Mai gani gare mu."

—
20:36
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

قَالَ قَدْ أُوتِيتَ سُؤْلَكَ يَـٰمُوسَىٰ﴿٣٦﴾

Ya ce: "Lalle ne, an bã ka rõƙonka, yã Mũsã!"

—
20:37
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 313

وَلَقَدْ مَنَنَّا عَلَيْكَ مَرَّةً أُخْرَىٰٓ﴿٣٧﴾

"Kuma lalle ne haƙĩƙa, Mun yi wata baiwa gare ka a wani lõkacin na dabam."

—
20:38
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

إِذْ أَوْحَيْنَآ إِلَىٰٓ أُمِّكَ مَا يُوحَىٰٓ﴿٣٨﴾

"A lõkacin da Muka yi wahayin abin da aka yi wahayi zuwa ga uwarka."

—
20:39
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

أَنِ ٱقْذِفِيهِ فِى ٱلتَّابُوتِ فَٱقْذِفِيهِ فِى ٱلْيَمِّ فَلْيُلْقِهِ ٱلْيَمُّ بِٱلسَّاحِلِ يَأْخُذْهُ عَدُوٌّ لِّى وَعَدُوٌّ لَّهُۥ ۚ وَأَلْقَيْتُ عَلَيْكَ مَحَبَّةً مِّنِّى وَلِتُصْنَعَ عَلَىٰ عَيْنِىٓ﴿٣٩﴾

"Cẽwa, Ki jẽfa shi a cikin akwatin nan, sa'an nan ki jẽfa shi a cikin kõgi, sa'an nan kogin ya jefa shi a gãɓa, wani maƙiyi Nãwa kuma maƙiyi nãsa ya ɗauke shi.' Kuma Na jẽfa wani so daga gare Ni a kanka. Kuma dõmin a riƙe ka da kyau a kan ganiNa."

—
20:40
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

إِذْ تَمْشِىٓ أُخْتُكَ فَتَقُولُ هَلْ أَدُلُّكُمْ عَلَىٰ مَن يَكْفُلُهُۥ ۖ فَرَجَعْنَـٰكَ إِلَىٰٓ أُمِّكَ كَىْ تَقَرَّ عَيْنُهَا وَلَا تَحْزَنَ ۚ وَقَتَلْتَ نَفْسًا فَنَجَّيْنَـٰكَ مِنَ ٱلْغَمِّ وَفَتَنَّـٰكَ فُتُونًا ۚ فَلَبِثْتَ سِنِينَ فِىٓ أَهْلِ مَدْيَنَ ثُمَّ جِئْتَ عَلَىٰ قَدَرٍ يَـٰمُوسَىٰ﴿٤٠﴾

"A sa'ad da 'yar'uwrka ke tafiya har ta ce, shin, in shiryar da ku ga wanda ke rẽnonsa?' Sai Muka mayar da kai zuwa ga uwarka dõmin idonta ya yi sanyi kuma bã zã ta yi baƙin ciki ba. Kuma kã kashe wani rai, sa'an nan Muka tsẽrar da kai daga baƙin ciki, kuma Muka fitine ka da waɗansu fitinõni. Sa'an nan ka zauna shẽkaru a cikin mutãnen Madyana. Sa'an nan kuma ka zo a kan wata ƙaddara, yã Mũsã!

—
20:41
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

وَٱصْطَنَعْتُكَ لِنَفْسِى﴿٤١﴾

"Kuma Na zãɓe ka dõmin Kaina."

—
20:42
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

ٱذْهَبْ أَنتَ وَأَخُوكَ بِـَٔايَـٰتِى وَلَا تَنِيَا فِى ذِكْرِى﴿٤٢﴾

"Ka tafi kai da ɗan'uwanka game da ãyõyiNa, kuma kada ku yi rauni ga ambatõNa."

—
20:43
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

ٱذْهَبَآ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ﴿٤٣﴾

"Ku tafi kũ biyu zuwa ga Fir'auna. Lalle shĩ ya ƙẽtare haddi (ga girman kai)."

—
20:44
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

فَقُولَا لَهُۥ قَوْلًا لَّيِّنًا لَّعَلَّهُۥ يَتَذَكَّرُ أَوْ يَخْشَىٰ﴿٤٤﴾

"Sai ku gaya masa magana mai laushi, tsammãninsa yanã tunãwa kõ kuwa ya ji tsõro."

—
20:45
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

قَالَا رَبَّنَآ إِنَّنَا نَخَافُ أَن يَفْرُطَ عَلَيْنَآ أَوْ أَن يَطْغَىٰ﴿٤٥﴾

Su biyu suka ce: "Ya Ubangijinmu! Lalle ne munã tsõron ya yi gaggawa a kanmu, kõ ya ƙẽtare haddi."

—
20:46
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

قَالَ لَا تَخَافَآ ۖ إِنَّنِى مَعَكُمَآ أَسْمَعُ وَأَرَىٰ﴿٤٦﴾

Ya ce: "Kada ku ji tsõro. Lalle Nĩ, Inã tãre da ku, Inaji, kuma Inã gani."

—
20:47
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

فَأْتِيَاهُ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولَا رَبِّكَ فَأَرْسِلْ مَعَنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ وَلَا تُعَذِّبْهُمْ ۖ قَدْ جِئْنَـٰكَ بِـَٔايَةٍ مِّن رَّبِّكَ ۖ وَٱلسَّلَـٰمُ عَلَىٰ مَنِ ٱتَّبَعَ ٱلْهُدَىٰٓ﴿٤٧﴾

"Sai ku jẽ masa sa'an nan ku ce, Lalle mũ, Manzanni biyune na Ubangijinka, sai ka saki Banĩ Isrã'ĩla tãre da mu. Kuma kada ka yi musu azãba. Haƙĩƙa mun zomaka da wata ãyã daga, Ubangijinka. Kuma aminci ya tabbata ga wanda ya bi shiriya."

—
20:48
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

إِنَّا قَدْ أُوحِىَ إِلَيْنَآ أَنَّ ٱلْعَذَابَ عَلَىٰ مَن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ﴿٤٨﴾

"Lalle mũ, haƙĩƙa, an yi wahayi zuwa gare mu, cẽwaazãba tanã a kan wanda ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya."

—
20:49
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

قَالَ فَمَن رَّبُّكُمَا يَـٰمُوسَىٰ﴿٤٩﴾

Ya ce: "To, wãne ne Ubangijinku? Ya Mũsã!"

—
20:50
Juz'i 16 · Hizbi 32 · Shafi 314

قَالَ رَبُّنَا ٱلَّذِىٓ أَعْطَىٰ كُلَّ شَىْءٍ خَلْقَهُۥ ثُمَّ هَدَىٰ﴿٥٠﴾

Ya ce: "Ubangijinmu Shi ne wanda Ya bai wa dukan kõme halittarsa, sa'an nan Ya shiryar."

—
Aya Da Ta GabataMaryamAya Mai ZuwaAl-Anbya