Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/60

الذاريات

Adh-Dhariyat

Zâriyât

Makkiyya·Ayoyi 60

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

51:1
Juz'i 26
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

وَٱلذَّٰرِيَـٰتِ ذَرْوًا﴿١﴾

Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

—
51:2
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

فَٱلْحَـٰمِلَـٰتِ وِقْرًا﴿٢﴾

Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

—
51:3
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

فَٱلْجَـٰرِيَـٰتِ يُسْرًا﴿٣﴾

Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.

—
51:4
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

فَٱلْمُقَسِّمَـٰتِ أَمْرًا﴿٤﴾

Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

—
51:5
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌ﴿٥﴾

Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

—
51:6
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 520

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٌ﴿٦﴾

Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

—
51:7
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلْحُبُكِ﴿٧﴾

Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).

—
51:8
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

إِنَّكُمْ لَفِى قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍ﴿٨﴾

Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

—
51:9
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ﴿٩﴾

Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

—
51:10
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

قُتِلَ ٱلْخَرَّٰصُونَ﴿١٠﴾

An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.

—
51:11
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

ٱلَّذِينَ هُمْ فِى غَمْرَةٍ سَاهُونَ﴿١١﴾

Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.

—
51:12
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

يَسْـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ ٱلدِّينِ﴿١٢﴾

Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"

—
51:13
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

يَوْمَ هُمْ عَلَى ٱلنَّارِ يُفْتَنُونَ﴿١٣﴾

Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.

—
51:14
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

ذُوقُوا۟ فِتْنَتَكُمْ هَـٰذَا ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تَسْتَعْجِلُونَ﴿١٤﴾

(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."

—
51:15
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

إِنَّ ٱلْمُتَّقِينَ فِى جَنَّـٰتٍ وَعُيُونٍ﴿١٥﴾

Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.

—
51:16
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ﴿١٦﴾

Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).

—
51:17
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

كَانُوا۟ قَلِيلًا مِّنَ ٱلَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ﴿١٧﴾

Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.

—
51:18
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَبِٱلْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ﴿١٨﴾

Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.

—
51:19
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَفِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ﴿١٩﴾

Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.

—
51:20
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَفِى ٱلْأَرْضِ ءَايَـٰتٌ لِّلْمُوقِنِينَ﴿٢٠﴾

Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.

—
51:21
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَفِىٓ أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ﴿٢١﴾

Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?

—
51:22
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

وَفِى ٱلسَّمَآءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ﴿٢٢﴾

Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.

—
51:23
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلْأَرْضِ إِنَّهُۥ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَآ أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ﴿٢٣﴾

To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,

—
51:24
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَٰهِيمَ ٱلْمُكْرَمِينَ﴿٢٤﴾

Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

—
51:25
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

إِذْ دَخَلُوا۟ عَلَيْهِ فَقَالُوا۟ سَلَـٰمًا ۖ قَالَ سَلَـٰمٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ﴿٢٥﴾

A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"

—
51:26
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهْلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍ﴿٢٦﴾

Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

—
51:27
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ﴿٢٧﴾

Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"

—
51:28
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً ۖ قَالُوا۟ لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَـٰمٍ عَلِيمٍ﴿٢٨﴾

Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

—
51:29
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

فَأَقْبَلَتِ ٱمْرَأَتُهُۥ فِى صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌ﴿٢٩﴾

Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"

—
51:30
Juz'i 26 · Hizbi 52 · Shafi 521

قَالُوا۟ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلْحَكِيمُ ٱلْعَلِيمُ﴿٣٠﴾

Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

—
51:31
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

۞ قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا ٱلْمُرْسَلُونَ﴿٣١﴾

(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"

—
51:32
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

قَالُوٓا۟ إِنَّآ أُرْسِلْنَآ إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ﴿٣٢﴾

Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.

—
51:33
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍ﴿٣٣﴾

"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).

—
51:34
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ﴿٣٤﴾

"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."

—
51:35
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلْمُؤْمِنِينَ﴿٣٥﴾

Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

—
51:36
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ ٱلْمُسْلِمِينَ﴿٣٦﴾

Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.

—
51:37
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَتَرَكْنَا فِيهَآ ءَايَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلْعَذَابَ ٱلْأَلِيمَ﴿٣٧﴾

Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.

—
51:38
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَفِى مُوسَىٰٓ إِذْ أَرْسَلْنَـٰهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَـٰنٍ مُّبِينٍ﴿٣٨﴾

Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

—
51:39
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِۦ وَقَالَ سَـٰحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ﴿٣٩﴾

Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"

—
51:40
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَأَخَذْنَـٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذْنَـٰهُمْ فِى ٱلْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌ﴿٤٠﴾

Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.

—
51:41
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَفِى عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلْعَقِيمَ﴿٤١﴾

Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

—
51:42
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

مَا تَذَرُ مِن شَىْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَٱلرَّمِيمِ﴿٤٢﴾

Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

—
51:43
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَفِى ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا۟ حَتَّىٰ حِينٍ﴿٤٣﴾

Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"

—
51:44
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَعَتَوْا۟ عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ ٱلصَّـٰعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ﴿٤٤﴾

Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.

—
51:45
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَمَا ٱسْتَطَـٰعُوا۟ مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا۟ مُنتَصِرِينَ﴿٤٥﴾

Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.

—
51:46
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا۟ قَوْمًا فَـٰسِقِينَ﴿٤٦﴾

Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.

—
51:47
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَٱلسَّمَآءَ بَنَيْنَـٰهَا بِأَيْي۟دٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ﴿٤٧﴾

Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.

—
51:48
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَٱلْأَرْضَ فَرَشْنَـٰهَا فَنِعْمَ ٱلْمَـٰهِدُونَ﴿٤٨﴾

Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,

—
51:49
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

وَمِن كُلِّ شَىْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ﴿٤٩﴾

Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.

—
51:50
Juz'i 27 · Hizbi 53 · Shafi 522

فَفِرُّوٓا۟ إِلَى ٱللَّهِ ۖ إِنِّى لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ﴿٥٠﴾

Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

—
Aya Da Ta GabataQafAya Mai ZuwaAt-Tur