Rahmân
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
ٱلرَّحْمَـٰنُ﴿١﴾
(Allah) Mai rahama.
—عَلَّمَ ٱلْقُرْءَانَ﴿٢﴾
Yã sanar da Alƙur'ani.
—خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ﴿٣﴾
Yã halitta mutum.
—عَلَّمَهُ ٱلْبَيَانَ﴿٤﴾
Yã sanar da shi bayãni (magana).
—ٱلشَّمْسُ وَٱلْقَمَرُ بِحُسْبَانٍ﴿٥﴾
Rãnã da watã a kan lissãfi suke.
—وَٱلنَّجْمُ وَٱلشَّجَرُ يَسْجُدَانِ﴿٦﴾
Kuma tsirrai mãsu yãɗo da itãce sunã tawãlu'i.
—وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلْمِيزَانَ﴿٧﴾
Kuma samã Ya ɗaukaka ta, Kuma Yã aza sikẽli.
—أَلَّا تَطْغَوْا۟ فِى ٱلْمِيزَانِ﴿٨﴾
Dõmin kada ku karkatar da sikẽlin.
—وَأَقِيمُوا۟ ٱلْوَزْنَ بِٱلْقِسْطِ وَلَا تُخْسِرُوا۟ ٱلْمِيزَانَ﴿٩﴾
Kuma ku daidaita awo da ãdalci, kuma kada ku rage sikẽlin.
—وَٱلْأَرْضَ وَضَعَهَا لِلْأَنَامِ﴿١٠﴾
Kuma ƙasã Yã aza ta dõmin tãlikai.
—فِيهَا فَـٰكِهَةٌ وَٱلنَّخْلُ ذَاتُ ٱلْأَكْمَامِ﴿١١﴾
A cikinta akwai 'ya'yan itãcen marmari da dabĩno mai kwasfa.
—وَٱلْحَبُّ ذُو ٱلْعَصْفِ وَٱلرَّيْحَانُ﴿١٢﴾
Da ƙwãya mai sõshiya da ƙamshi.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿١٣﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangjinku kuke ƙaryatãwa?
—خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِن صَلْصَـٰلٍ كَٱلْفَخَّارِ﴿١٤﴾
Yã halitta mutum daga ƙẽkasasshen yumɓu kumar kasko.
—وَخَلَقَ ٱلْجَآنَّ مِن مَّارِجٍ مِّن نَّارٍ﴿١٥﴾
Kuma ya halitta aljani daga bira daga wutã.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿١٦﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—رَبُّ ٱلْمَشْرِقَيْنِ وَرَبُّ ٱلْمَغْرِبَيْنِ﴿١٧﴾
Ubangjin mafita biyu na rãnã, kuma Ubangijin mafãɗã biyu na rãnã.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿١٨﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—مَرَجَ ٱلْبَحْرَيْنِ يَلْتَقِيَانِ﴿١٩﴾
Yã garwaya tẽku biyu (ruwan dãɗi da na zartsi) sunã haɗuwa.
—بَيْنَهُمَا بَرْزَخٌ لَّا يَبْغِيَانِ﴿٢٠﴾
A tsakãninsu akwai shãmaki, bã za su ƙetare haddi ba.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٢١﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—يَخْرُجُ مِنْهُمَا ٱللُّؤْلُؤُ وَٱلْمَرْجَانُ﴿٢٢﴾
Lu'ulu'u da murjãni na fita daga gare su.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٢٣﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—وَلَهُ ٱلْجَوَارِ ٱلْمُنشَـَٔاتُ فِى ٱلْبَحْرِ كَٱلْأَعْلَـٰمِ﴿٢٤﴾
Kuma Yanã da manyan jirãge, waɗanda ake ƙãgãwa a cikin tẽku kamar manyan duwãtsu.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٢٥﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—كُلُّ مَنْ عَلَيْهَا فَانٍ﴿٢٦﴾
Dukkan wanda ke kanta mai ƙãrẽwa ne.
—وَيَبْقَىٰ وَجْهُ رَبِّكَ ذُو ٱلْجَلَـٰلِ وَٱلْإِكْرَامِ﴿٢٧﴾
Kuma Fuskarar Ubangijinka, Mai girman Jalala da karimci, ita ce take wanzuwa.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٢٨﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—يَسْـَٔلُهُۥ مَن فِى ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ ۚ كُلَّ يَوْمٍ هُوَ فِى شَأْنٍ﴿٢٩﴾
wanda ke a cikin sammai da ƙasã yanã rõƙon Sa (Allah), a kullum Allah na a cikin wani sha'ani.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٣٠﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—سَنَفْرُغُ لَكُمْ أَيُّهَ ٱلثَّقَلَانِ﴿٣١﴾
Zã mu ɗauki lõkaci sabõda ku, yã kũ mãsu nauyin halitta biyu!
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٣٢﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—يَـٰمَعْشَرَ ٱلْجِنِّ وَٱلْإِنسِ إِنِ ٱسْتَطَعْتُمْ أَن تَنفُذُوا۟ مِنْ أَقْطَارِ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ فَٱنفُذُوا۟ ۚ لَا تَنفُذُونَ إِلَّا بِسُلْطَـٰنٍ﴿٣٣﴾
Ya jama'ar aljannu da mutãne! Idan kunã iya zarcẽwa daga sãsannin sammai da ƙasã to ku zarce. Bã za ku iya zarcẽwaba fãce da wani dalĩli.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٣٤﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—يُرْسَلُ عَلَيْكُمَا شُوَاظٌ مِّن نَّارٍ وَنُحَاسٌ فَلَا تَنتَصِرَانِ﴿٣٥﴾
Anã sako wani harshe daga wata wutã a kanku, da narkakkiyar tagulla. To, bã zã ku nẽmi taimako ba?
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٣٦﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—فَإِذَا ٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ وَرْدَةً كَٱلدِّهَانِ﴿٣٧﴾
Sa'an nan idan sama ta tsãge kuma ta zama jã kamar jar fãta.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٣٨﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—فَيَوْمَئِذٍ لَّا يُسْـَٔلُ عَن ذَنۢبِهِۦٓ إِنسٌ وَلَا جَآنٌّ﴿٣٩﴾
To, a ran nan bã zã a tambayi wani mutum laifinsa ba, kuma haka aljani.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٤٠﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—يُعْرَفُ ٱلْمُجْرِمُونَ بِسِيمَـٰهُمْ فَيُؤْخَذُ بِٱلنَّوَٰصِى وَٱلْأَقْدَامِ﴿٤١﴾
zã a iya sanin mãsu laifi da alãmarsu, sabõda haka sai a kãma kwarkaɗarsu da sãwãyensu.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٤٢﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—هَـٰذِهِۦ جَهَنَّمُ ٱلَّتِى يُكَذِّبُ بِهَا ٱلْمُجْرِمُونَ﴿٤٣﴾
Wannan Jahannama ce wadda mãsu laifi ke ƙaryatãwa game da ita.
—يَطُوفُونَ بَيْنَهَا وَبَيْنَ حَمِيمٍ ءَانٍ﴿٤٤﴾
Sunã kẽwaya a tsakaninta da ruwan ɗimi mai tsananin tafasa.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٤٥﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—وَلِمَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ﴿٤٦﴾
Kuma wanda ya ji tsõron tsayãwa a gaba ga Ubangijinsa yanã da Aljanna biyu.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٤٧﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—ذَوَاتَآ أَفْنَانٍ﴿٤٨﴾
Mãsu rassan itãce.
—فَبِأَىِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ﴿٤٩﴾
To, sabõda wanne daga ni'imõmin Ubangijinku, kuke ƙaryatãwa?
—فِيهِمَا عَيْنَانِ تَجْرِيَانِ﴿٥٠﴾
A cikinsu akwai marẽmari biyu sunã gudãna.
—