Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/52

القلم

Al-Qalam

Kalem

Makkiyya·Ayoyi 52

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

68:1
Juz'i 29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

نٓ ۚ وَٱلْقَلَمِ وَمَا يَسْطُرُونَ﴿١﴾

Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.

—
68:2
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

مَآ أَنتَ بِنِعْمَةِ رَبِّكَ بِمَجْنُونٍ﴿٢﴾

Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.

—
68:3
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

وَإِنَّ لَكَ لَأَجْرًا غَيْرَ مَمْنُونٍ﴿٣﴾

Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.

—
68:4
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٍ﴿٤﴾

Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.

—
68:5
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

فَسَتُبْصِرُ وَيُبْصِرُونَ﴿٥﴾

Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.

—
68:6
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

بِأَييِّكُمُ ٱلْمَفْتُونُ﴿٦﴾

Ga wanenku haukã take.

—
68:7
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعْلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعْلَمُ بِٱلْمُهْتَدِينَ﴿٧﴾

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkinSa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.

—
68:8
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

فَلَا تُطِعِ ٱلْمُكَذِّبِينَ﴿٨﴾

Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.

—
68:9
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

وَدُّوا۟ لَوْ تُدْهِنُ فَيُدْهِنُونَ﴿٩﴾

Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.

—
68:10
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

وَلَا تُطِعْ كُلَّ حَلَّافٍ مَّهِينٍ﴿١٠﴾

Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.

—
68:11
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

هَمَّازٍ مَّشَّآءٍۭ بِنَمِيمٍ﴿١١﴾

Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.

—
68:12
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

مَّنَّاعٍ لِّلْخَيْرِ مُعْتَدٍ أَثِيمٍ﴿١٢﴾

Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.

—
68:13
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

عُتُلٍّۭ بَعْدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ﴿١٣﴾

Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).

—
68:14
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

أَن كَانَ ذَا مَالٍ وَبَنِينَ﴿١٤﴾

Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.

—
68:15
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

إِذَا تُتْلَىٰ عَلَيْهِ ءَايَـٰتُنَا قَالَ أَسَـٰطِيرُ ٱلْأَوَّلِينَ﴿١٥﴾

Idan ana karanta masa ãyõyinMu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."

—
68:16
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 564

سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلْخُرْطُومِ﴿١٦﴾

Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.

—
68:17
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

إِنَّا بَلَوْنَـٰهُمْ كَمَا بَلَوْنَآ أَصْحَـٰبَ ٱلْجَنَّةِ إِذْ أَقْسَمُوا۟ لَيَصْرِمُنَّهَا مُصْبِحِينَ﴿١٧﴾

Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.

—
68:18
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

وَلَا يَسْتَثْنُونَ﴿١٨﴾

Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.

—
68:19
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَطَافَ عَلَيْهَا طَآئِفٌ مِّن رَّبِّكَ وَهُمْ نَآئِمُونَ﴿١٩﴾

Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.

—
68:20
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَأَصْبَحَتْ كَٱلصَّرِيمِ﴿٢٠﴾

Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.

—
68:21
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَتَنَادَوْا۟ مُصْبِحِينَ﴿٢١﴾

Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.

—
68:22
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَنِ ٱغْدُوا۟ عَلَىٰ حَرْثِكُمْ إِن كُنتُمْ صَـٰرِمِينَ﴿٢٢﴾

Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.

—
68:23
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَٱنطَلَقُوا۟ وَهُمْ يَتَخَـٰفَتُونَ﴿٢٣﴾

Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).

—
68:24
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَن لَّا يَدْخُلَنَّهَا ٱلْيَوْمَ عَلَيْكُم مِّسْكِينٌ﴿٢٤﴾

"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"

—
68:25
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

وَغَدَوْا۟ عَلَىٰ حَرْدٍ قَـٰدِرِينَ﴿٢٥﴾

Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.

—
68:26
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَلَمَّا رَأَوْهَا قَالُوٓا۟ إِنَّا لَضَآلُّونَ﴿٢٦﴾

Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"

—
68:27
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

بَلْ نَحْنُ مَحْرُومُونَ﴿٢٧﴾

"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."

—
68:28
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

قَالَ أَوْسَطُهُمْ أَلَمْ أَقُل لَّكُمْ لَوْلَا تُسَبِّحُونَ﴿٢٨﴾

Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"

—
68:29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

قَالُوا۟ سُبْحَـٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَـٰلِمِينَ﴿٢٩﴾

Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."

—
68:30
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَلَـٰوَمُونَ﴿٣٠﴾

Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.

—
68:31
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

قَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَـٰغِينَ﴿٣١﴾

Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."

—
68:32
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبْدِلَنَا خَيْرًا مِّنْهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ﴿٣٢﴾

"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."

—
68:33
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

كَذَٰلِكَ ٱلْعَذَابُ ۖ وَلَعَذَابُ ٱلْـَٔاخِرَةِ أَكْبَرُ ۚ لَوْ كَانُوا۟ يَعْلَمُونَ﴿٣٣﴾

Haka dai azãbar take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.

—
68:34
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمْ جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ﴿٣٤﴾

Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.

—
68:35
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَفَنَجْعَلُ ٱلْمُسْلِمِينَ كَٱلْمُجْرِمِينَ﴿٣٥﴾

Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?

—
68:36
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

مَا لَكُمْ كَيْفَ تَحْكُمُونَ﴿٣٦﴾

Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?

—
68:37
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَمْ لَكُمْ كِتَـٰبٌ فِيهِ تَدْرُسُونَ﴿٣٧﴾

Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?

—
68:38
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

إِنَّ لَكُمْ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ﴿٣٨﴾

Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?

—
68:39
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَمْ لَكُمْ أَيْمَـٰنٌ عَلَيْنَا بَـٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوْمِ ٱلْقِيَـٰمَةِ ۙ إِنَّ لَكُمْ لَمَا تَحْكُمُونَ﴿٣٩﴾

Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kanMu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?

—
68:40
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

سَلْهُمْ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ﴿٤٠﴾

Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?

—
68:41
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

أَمْ لَهُمْ شُرَكَآءُ فَلْيَأْتُوا۟ بِشُرَكَآئِهِمْ إِن كَانُوا۟ صَـٰدِقِينَ﴿٤١﴾

Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.

—
68:42
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 565

يَوْمَ يُكْشَفُ عَن سَاقٍ وَيُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسْتَطِيعُونَ﴿٤٢﴾

Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujũda, sai bã zã su iyãwa ba.

—
68:43
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۖ وَقَدْ كَانُوا۟ يُدْعَوْنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمْ سَـٰلِمُونَ﴿٤٣﴾

Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).

—
68:44
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

فَذَرْنِى وَمَن يُكَذِّبُ بِهَـٰذَا ٱلْحَدِيثِ ۖ سَنَسْتَدْرِجُهُم مِّنْ حَيْثُ لَا يَعْلَمُونَ﴿٤٤﴾

Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.

—
68:45
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

وَأُمْلِى لَهُمْ ۚ إِنَّ كَيْدِى مَتِينٌ﴿٤٥﴾

Ina jinkirtã musu, lalle kaidiNa mai ƙarfi ne.

—
68:46
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

أَمْ تَسْـَٔلُهُمْ أَجْرًا فَهُم مِّن مَّغْرَمٍ مُّثْقَلُونَ﴿٤٦﴾

Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?

—
68:47
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

أَمْ عِندَهُمُ ٱلْغَيْبُ فَهُمْ يَكْتُبُونَ﴿٤٧﴾

Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?

—
68:48
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

فَٱصْبِرْ لِحُكْمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلْحُوتِ إِذْ نَادَىٰ وَهُوَ مَكْظُومٌ﴿٤٨﴾

Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.

—
68:49
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

لَّوْلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعْمَةٌ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلْعَرَآءِ وَهُوَ مَذْمُومٌ﴿٤٩﴾

Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.

—
68:50
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

فَٱجْتَبَـٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ﴿٥٠﴾

Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.

—
Aya Da Ta GabataAl-MulkAya Mai ZuwaAl-Haqqah