Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/44

المعارج

Al-Ma'arij

Meâric

Makkiyya·Ayoyi 44

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

70:1
Juz'i 29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍ وَاقِعٍ﴿١﴾

Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

—
70:2
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

لِّلْكَـٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌ﴿٢﴾

Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

—
70:3
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ﴿٣﴾

Daga Allah Mai matãkala.

—
70:4
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

تَعْرُجُ ٱلْمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍ﴿٤﴾

Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

—
70:5
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

فَٱصْبِرْ صَبْرًا جَمِيلًا﴿٥﴾

Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

—
70:6
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًا﴿٦﴾

Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

—
70:7
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَنَرَىٰهُ قَرِيبًا﴿٧﴾

Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

—
70:8
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ﴿٨﴾

Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

—
70:9
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ﴿٩﴾

Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

—
70:10
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًا﴿١٠﴾

Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

—
70:11
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ﴿١١﴾

Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

—
70:12
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ﴿١٢﴾

Da matarsa da ɗan'uwansa.

—
70:13
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ﴿١٣﴾

Da danginsa, mãsu tattarã shi.

—
70:14
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًا ثُمَّ يُنجِيهِ﴿١٤﴾

Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

—
70:15
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

—
70:16
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

نَزَّاعَةً لِّلشَّوَىٰ﴿١٦﴾

Mai twãle fãtar goshi.

—
70:17
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ﴿١٧﴾

Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

—
70:18
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ﴿١٨﴾

Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

—
70:19
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

۞ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا﴿١٩﴾

Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

—
70:20
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًا﴿٢٠﴾

Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

—
70:21
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا﴿٢١﴾

Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

—
70:22
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ﴿٢٢﴾

Sai mãsu yin salla,

—
70:23
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ﴿٢٣﴾

Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

—
70:24
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّ مَّعْلُومٌ﴿٢٤﴾

Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

—
70:25
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ﴿٢٥﴾

Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

—
70:26
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ﴿٢٦﴾

Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

—
70:27
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ﴿٢٧﴾

Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

—
70:28
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍ﴿٢٨﴾

Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

—
70:29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَـٰفِظُونَ﴿٢٩﴾

Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

—
70:30
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَـٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ﴿٣٠﴾

Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

—
70:31
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ﴿٣١﴾

To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

—
70:32
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَـٰنَـٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ﴿٣٢﴾

Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

—
70:33
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَـٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ﴿٣٣﴾

Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

—
70:34
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ﴿٣٤﴾

Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

—
70:35
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

أُو۟لَـٰٓئِكَ فِى جَنَّـٰتٍ مُّكْرَمُونَ﴿٣٥﴾

Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

—
70:36
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ﴿٣٦﴾

Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

—
70:37
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ﴿٣٧﴾

Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

—
70:38
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍ﴿٣٨﴾

Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

—
70:39
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ﴿٣٩﴾

A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

—
70:40
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 569

فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَـٰرِقِ وَٱلْمَغَـٰرِبِ إِنَّا لَقَـٰدِرُونَ﴿٤٠﴾

Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

—
70:41
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 570

عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ﴿٤١﴾

Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

—
70:42
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 570

فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَـٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ﴿٤٢﴾

Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

—
70:43
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 570

يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍ يُوفِضُونَ﴿٤٣﴾

Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

—
70:44
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 570

خَـٰشِعَةً أَبْصَـٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ﴿٤٤﴾

Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)

—
Aya Da Ta GabataAl-HaqqahAya Mai ZuwaNuh