Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/19

العلق

Al-'Alaq

Alâk

Makkiyya·Ayoyi 19

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

96:1
Juz'i 30
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

ٱقْرَأْ بِٱسْمِ رَبِّكَ ٱلَّذِى خَلَقَ﴿١﴾

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.

—
96:2
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

خَلَقَ ٱلْإِنسَـٰنَ مِنْ عَلَقٍ﴿٢﴾

Ya hahitta mutum daga gudan jini.

—
96:3
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

ٱقْرَأْ وَرَبُّكَ ٱلْأَكْرَمُ﴿٣﴾

Ka yi karatu, kuma UbangiJinka shi ne Mafi karimci.

—
96:4
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

ٱلَّذِى عَلَّمَ بِٱلْقَلَمِ﴿٤﴾

Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.

—
96:5
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

عَلَّمَ ٱلْإِنسَـٰنَ مَا لَمْ يَعْلَمْ﴿٥﴾

Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.

—
96:6
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

كَلَّآ إِنَّ ٱلْإِنسَـٰنَ لَيَطْغَىٰٓ﴿٦﴾

A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).

—
96:7
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

أَن رَّءَاهُ ٱسْتَغْنَىٰٓ﴿٧﴾

Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.

—
96:8
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجْعَىٰٓ﴿٨﴾

Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.

—
96:9
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

أَرَءَيْتَ ٱلَّذِى يَنْهَىٰ﴿٩﴾

Shin, kã ga wanda ke hana.

—
96:10
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

عَبْدًا إِذَا صَلَّىٰٓ﴿١٠﴾

Bãwã idan yã yi salla?

—
96:11
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

أَرَءَيْتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلْهُدَىٰٓ﴿١١﴾

Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?

—
96:12
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 597

أَوْ أَمَرَ بِٱلتَّقْوَىٰٓ﴿١٢﴾

Ko ya yi umurni da taƙawa?

—
96:13
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

أَرَءَيْتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ﴿١٣﴾

Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?

—
96:14
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

أَلَمْ يَعْلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ﴿١٤﴾

Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?

—
96:15
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

كَلَّا لَئِن لَّمْ يَنتَهِ لَنَسْفَعًۢا بِٱلنَّاصِيَةِ﴿١٥﴾

A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.

—
96:16
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

نَاصِيَةٍ كَـٰذِبَةٍ خَاطِئَةٍ﴿١٦﴾

Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.

—
96:17
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

فَلْيَدْعُ نَادِيَهُۥ﴿١٧﴾

Sai ya kirayi ƙungiyarsa.

—
96:18
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

سَنَدْعُ ٱلزَّبَانِيَةَ﴿١٨﴾

Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).

—
96:19۩
Juz'i 30 · Hizbi 60 · Shafi 598

كَلَّا لَا تُطِعْهُ وَٱسْجُدْ وَٱقْتَرِب ۩﴿١٩﴾

A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u, kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).

—
Aya Da Ta GabataAt-TinAya Mai ZuwaAl-Qadr