Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/227

الشعراء

Ash-Shu'ara

Şuarâ

Makkiyya·Ayoyi 227

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

26:1
Juz'i 19
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

طسٓمٓ﴿١﴾

¦. S̃. M̃.

—
26:2
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

تِلْكَ ءَايَـٰتُ ٱلْكِتَـٰبِ ٱلْمُبِينِ﴿٢﴾

Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

—
26:3
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

لَعَلَّكَ بَـٰخِعٌ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ﴿٣﴾

Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!

—
26:4
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةً فَظَلَّتْ أَعْنَـٰقُهُمْ لَهَا خَـٰضِعِينَ﴿٤﴾

Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

—
26:5
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ ٱلرَّحْمَـٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا۟ عَنْهُ مُعْرِضِينَ﴿٥﴾

Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

—
26:6
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

فَقَدْ كَذَّبُوا۟ فَسَيَأْتِيهِمْ أَنۢبَـٰٓؤُا۟ مَا كَانُوا۟ بِهِۦ يَسْتَهْزِءُونَ﴿٦﴾

To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

—
26:7
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

أَوَلَمْ يَرَوْا۟ إِلَى ٱلْأَرْضِ كَمْ أَنۢبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍ﴿٧﴾

Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

—
26:8
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَـَٔايَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ﴿٨﴾

Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

—
26:9
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ﴿٩﴾

Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

—
26:10
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئْتِ ٱلْقَوْمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ﴿١٠﴾

Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

—
26:11
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ﴿١١﴾

"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

—
26:12
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

قَالَ رَبِّ إِنِّىٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ﴿١٢﴾

Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

—
26:13
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَيَضِيقُ صَدْرِى وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِى فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَـٰرُونَ﴿١٣﴾

"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

—
26:14
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَلَهُمْ عَلَىَّ ذَنۢبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ﴿١٤﴾

"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

—
26:15
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

قَالَ كَلَّا ۖ فَٱذْهَبَا بِـَٔايَـٰتِنَآ ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ﴿١٥﴾

Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

—
26:16
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿١٦﴾

"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

—
26:17
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ﴿١٧﴾

"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

—
26:18
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ﴿١٨﴾

Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

—
26:19
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 367

وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ ٱلَّتِى فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلْكَـٰفِرِينَ﴿١٩﴾

"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

—
26:20
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ فَعَلْتُهَآ إِذًا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ﴿٢٠﴾

Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."

—
26:21
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِى رَبِّى حُكْمًا وَجَعَلَنِى مِنَ ٱلْمُرْسَلِينَ﴿٢١﴾

"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

—
26:22
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَىَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ﴿٢٢﴾

"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

—
26:23
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿٢٣﴾

Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

—
26:24
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ﴿٢٤﴾

Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

—
26:25
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُۥٓ أَلَا تَسْتَمِعُونَ﴿٢٥﴾

Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

—
26:26
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلْأَوَّلِينَ﴿٢٦﴾

Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

—
26:27
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِىٓ أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌ﴿٢٧﴾

Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

—
26:28
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ رَبُّ ٱلْمَشْرِقِ وَٱلْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَآ ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ﴿٢٨﴾

Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

—
26:29
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذْتَ إِلَـٰهًا غَيْرِى لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ ٱلْمَسْجُونِينَ﴿٢٩﴾

Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

—
26:30
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَىْءٍ مُّبِينٍ﴿٣٠﴾

Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

—
26:31
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ فَأْتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ﴿٣١﴾

Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

—
26:32
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌ﴿٣٢﴾

Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

—
26:33
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِىَ بَيْضَآءُ لِلنَّـٰظِرِينَ﴿٣٣﴾

Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

—
26:34
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُۥٓ إِنَّ هَـٰذَا لَسَـٰحِرٌ عَلِيمٌ﴿٣٤﴾

(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

—
26:35
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِۦ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ﴿٣٥﴾

"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

—
26:36
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

قَالُوٓا۟ أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَٱبْعَثْ فِى ٱلْمَدَآئِنِ حَـٰشِرِينَ﴿٣٦﴾

Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

—
26:37
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍ﴿٣٧﴾

"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

—
26:38
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَـٰتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ﴿٣٨﴾

Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

—
26:39
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 368

وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ﴿٣٩﴾

Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

—
26:40
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُوا۟ هُمُ ٱلْغَـٰلِبِينَ﴿٤٠﴾

"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

—
26:41
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُوا۟ لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ ٱلْغَـٰلِبِينَ﴿٤١﴾

To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

—
26:42
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ ٱلْمُقَرَّبِينَ﴿٤٢﴾

Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

—
26:43
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلْقُوا۟ مَآ أَنتُم مُّلْقُونَ﴿٤٣﴾

Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

—
26:44
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

فَأَلْقَوْا۟ حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا۟ بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ ٱلْغَـٰلِبُونَ﴿٤٤﴾

Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

—
26:45
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِىَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ﴿٤٥﴾

Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

—
26:46
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

فَأُلْقِىَ ٱلسَّحَرَةُ سَـٰجِدِينَ﴿٤٦﴾

Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

—
26:47
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

قَالُوٓا۟ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿٤٧﴾

Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

—
26:48
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

رَبِّ مُوسَىٰ وَهَـٰرُونَ﴿٤٨﴾

"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

—
26:49
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

قَالَ ءَامَنتُمْ لَهُۥ قَبْلَ أَنْ ءَاذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِى عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَـٰفٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ﴿٤٩﴾

Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

—
26:50
Juz'i 19 · Hizbi 37 · Shafi 369

قَالُوا۟ لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ﴿٥٠﴾

Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

—
Aya Da Ta GabataAl-FurqanAya Mai ZuwaAn-Naml