Sâffât
بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ
وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفًّا﴿١﴾
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
—فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجْرًا﴿٢﴾
Sa'an nan mãsu yin tsãwa dõmin gargaɗi.
—فَٱلتَّـٰلِيَـٰتِ ذِكْرًا﴿٣﴾
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
—إِنَّ إِلَـٰهَكُمْ لَوَٰحِدٌ﴿٤﴾
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
—رَّبُّ ٱلسَّمَـٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا وَرَبُّ ٱلْمَشَـٰرِقِ﴿٥﴾
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
—إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنْيَا بِزِينَةٍ ٱلْكَوَاكِبِ﴿٦﴾
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
—وَحِفْظًا مِّن كُلِّ شَيْطَـٰنٍ مَّارِدٍ﴿٧﴾
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
—لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلْمَلَإِ ٱلْأَعْلَىٰ وَيُقْذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٍ﴿٨﴾
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
—دُحُورًا ۖ وَلَهُمْ عَذَابٌ وَاصِبٌ﴿٩﴾
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
—إِلَّا مَنْ خَطِفَ ٱلْخَطْفَةَ فَأَتْبَعَهُۥ شِهَابٌ ثَاقِبٌ﴿١٠﴾
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
—فَٱسْتَفْتِهِمْ أَهُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَم مَّنْ خَلَقْنَآ ۚ إِنَّا خَلَقْنَـٰهُم مِّن طِينٍ لَّازِبٍۭ﴿١١﴾
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
—بَلْ عَجِبْتَ وَيَسْخَرُونَ﴿١٢﴾
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
—وَإِذَا ذُكِّرُوا۟ لَا يَذْكُرُونَ﴿١٣﴾
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
—وَإِذَا رَأَوْا۟ ءَايَةً يَسْتَسْخِرُونَ﴿١٤﴾
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
—وَقَالُوٓا۟ إِنْ هَـٰذَآ إِلَّا سِحْرٌ مُّبِينٌ﴿١٥﴾
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
—أَءِذَا مِتْنَا وَكُنَّا تُرَابًا وَعِظَـٰمًا أَءِنَّا لَمَبْعُوثُونَ﴿١٦﴾
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
—أَوَءَابَآؤُنَا ٱلْأَوَّلُونَ﴿١٧﴾
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
—قُلْ نَعَمْ وَأَنتُمْ دَٰخِرُونَ﴿١٨﴾
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
—فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌ وَٰحِدَةٌ فَإِذَا هُمْ يَنظُرُونَ﴿١٩﴾
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
—وَقَالُوا۟ يَـٰوَيْلَنَا هَـٰذَا يَوْمُ ٱلدِّينِ﴿٢٠﴾
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
—هَـٰذَا يَوْمُ ٱلْفَصْلِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ﴿٢١﴾
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
—۞ ٱحْشُرُوا۟ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوا۟ وَأَزْوَٰجَهُمْ وَمَا كَانُوا۟ يَعْبُدُونَ﴿٢٢﴾
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
—مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهْدُوهُمْ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلْجَحِيمِ﴿٢٣﴾
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
—وَقِفُوهُمْ ۖ إِنَّهُم مَّسْـُٔولُونَ﴿٢٤﴾
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
—مَا لَكُمْ لَا تَنَاصَرُونَ﴿٢٥﴾
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
—بَلْ هُمُ ٱلْيَوْمَ مُسْتَسْلِمُونَ﴿٢٦﴾
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
—وَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ﴿٢٧﴾
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
—قَالُوٓا۟ إِنَّكُمْ كُنتُمْ تَأْتُونَنَا عَنِ ٱلْيَمِينِ﴿٢٨﴾
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
—قَالُوا۟ بَل لَّمْ تَكُونُوا۟ مُؤْمِنِينَ﴿٢٩﴾
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
—وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيْكُم مِّن سُلْطَـٰنٍۭ ۖ بَلْ كُنتُمْ قَوْمًا طَـٰغِينَ﴿٣٠﴾
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
—فَحَقَّ عَلَيْنَا قَوْلُ رَبِّنَآ ۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ﴿٣١﴾
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
—فَأَغْوَيْنَـٰكُمْ إِنَّا كُنَّا غَـٰوِينَ﴿٣٢﴾
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
—فَإِنَّهُمْ يَوْمَئِذٍ فِى ٱلْعَذَابِ مُشْتَرِكُونَ﴿٣٣﴾
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
—إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفْعَلُ بِٱلْمُجْرِمِينَ﴿٣٤﴾
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
—إِنَّهُمْ كَانُوٓا۟ إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَآ إِلَـٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ﴿٣٥﴾
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
—وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓا۟ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٍ مَّجْنُونٍۭ﴿٣٦﴾
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
—بَلْ جَآءَ بِٱلْحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلْمُرْسَلِينَ﴿٣٧﴾
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
—إِنَّكُمْ لَذَآئِقُوا۟ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَلِيمِ﴿٣٨﴾
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
—وَمَا تُجْزَوْنَ إِلَّا مَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ﴿٣٩﴾
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
—إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلْمُخْلَصِينَ﴿٤٠﴾
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
—أُو۟لَـٰٓئِكَ لَهُمْ رِزْقٌ مَّعْلُومٌ﴿٤١﴾
Waɗannan sunã da abinci sananne.
—فَوَٰكِهُ ۖ وَهُم مُّكْرَمُونَ﴿٤٢﴾
'Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
—فِى جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ﴿٤٣﴾
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
—عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَـٰبِلِينَ﴿٤٤﴾
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
—يُطَافُ عَلَيْهِم بِكَأْسٍ مِّن مَّعِينٍۭ﴿٤٥﴾
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
—بَيْضَآءَ لَذَّةٍ لِّلشَّـٰرِبِينَ﴿٤٦﴾
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
—لَا فِيهَا غَوْلٌ وَلَا هُمْ عَنْهَا يُنزَفُونَ﴿٤٧﴾
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
—وَعِندَهُمْ قَـٰصِرَٰتُ ٱلطَّرْفِ عِينٌ﴿٤٨﴾
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
—كَأَنَّهُنَّ بَيْضٌ مَّكْنُونٌ﴿٤٩﴾
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
—فَأَقْبَلَ بَعْضُهُمْ عَلَىٰ بَعْضٍ يَتَسَآءَلُونَ﴿٥٠﴾
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
—