Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/42

عبس

Abasa

Abese

Makkiyya·Ayoyi 42

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

80:1
Juz'i 30
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ﴿١﴾

Yã game huska kuma ya jũya bãya.

—
80:2
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ﴿٢﴾

Sabõda makãho yã je masa.

—
80:3
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ﴿٣﴾

To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

—
80:4
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ﴿٤﴾

Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

—
80:5
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ﴿٥﴾

Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

—
80:6
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ﴿٦﴾

Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

—
80:7
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ﴿٧﴾

To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

—
80:8
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ﴿٨﴾

Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

—
80:9
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَهُوَ يَخْشَىٰ﴿٩﴾

Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

—
80:10
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ﴿١٠﴾

Kai kuma kã shagala ga barinsa!

—
80:11
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌ﴿١١﴾

A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

—
80:12
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ﴿١٢﴾

Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

—
80:13
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فِى صُحُفٍ مُّكَرَّمَةٍ﴿١٣﴾

(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

—
80:14
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

مَّرْفُوعَةٍ مُّطَهَّرَةٍۭ﴿١٤﴾

Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

—
80:15
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

بِأَيْدِى سَفَرَةٍ﴿١٥﴾

A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

—
80:16
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

كِرَامٍۭ بَرَرَةٍ﴿١٦﴾

Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

—
80:17
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

قُتِلَ ٱلْإِنسَـٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ﴿١٧﴾

An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

—
80:18
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ﴿١٨﴾

Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

—
80:19
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ﴿١٩﴾

Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

—
80:20
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ﴿٢٠﴾

Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

—
80:21
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ﴿٢١﴾

Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

—
80:22
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ﴿٢٢﴾

Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

—
80:23
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ﴿٢٣﴾

Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

—
80:24
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَـٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ﴿٢٤﴾

To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

—
80:25
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّا﴿٢٥﴾

Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

—
80:26
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّا﴿٢٦﴾

Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

—
80:27
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّا﴿٢٧﴾

Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

—
80:28
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَعِنَبًا وَقَضْبًا﴿٢٨﴾

Da inabi da ciyãwa.

—
80:29
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَزَيْتُونًا وَنَخْلًا﴿٢٩﴾

Da zaitũni da itãcen dabĩno.

—
80:30
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَحَدَآئِقَ غُلْبًا﴿٣٠﴾

Da lambuna, mãsu yawan itãce.

—
80:31
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَفَـٰكِهَةً وَأَبًّا﴿٣١﴾

Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

—
80:32
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

مَّتَـٰعًا لَّكُمْ وَلِأَنْعَـٰمِكُمْ﴿٣٢﴾

Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

—
80:33
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ﴿٣٣﴾

To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

—
80:34
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ﴿٣٤﴾

Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

—
80:35
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ﴿٣٥﴾

Da uwarsa da ubansa.

—
80:36
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَصَـٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ﴿٣٦﴾

Da mãtarsa da ɗiyansa.

—
80:37
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

لِكُلِّ ٱمْرِئٍ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍ شَأْنٌ يُغْنِيهِ﴿٣٧﴾

Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

—
80:38
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ مُّسْفِرَةٌ﴿٣٨﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

—
80:39
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

ضَاحِكَةٌ مُّسْتَبْشِرَةٌ﴿٣٩﴾

Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

—
80:40
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 585

وَوُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌ﴿٤٠﴾

Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

—
80:41
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ﴿٤١﴾

Baƙi zai rufe su.

—
80:42
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

أُو۟لَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ﴿٤٢﴾

Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

—
Aya Da Ta GabataAn-Nazi'atAya Mai ZuwaAt-Takwir