Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/29

التكوير

At-Takwir

Tekvîr

Makkiyya·Ayoyi 29

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

81:1
Juz'i 30
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

إِذَا ٱلشَّمْسُ كُوِّرَتْ﴿١﴾

Idan rãna aka shafe haskenta

—
81:2
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتْ﴿٢﴾

Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

—
81:3
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْجِبَالُ سُيِّرَتْ﴿٣﴾

Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

—
81:4
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْعِشَارُ عُطِّلَتْ﴿٤﴾

Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

—
81:5
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْوُحُوشُ حُشِرَتْ﴿٥﴾

Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

—
81:6
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْبِحَارُ سُجِّرَتْ﴿٦﴾

Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

—
81:7
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتْ﴿٧﴾

Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

—
81:8
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْمَوْءُۥدَةُ سُئِلَتْ﴿٨﴾

Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

—
81:9
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

بِأَىِّ ذَنۢبٍ قُتِلَتْ﴿٩﴾

"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

—
81:10
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتْ﴿١٠﴾

Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

—
81:11
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتْ﴿١١﴾

Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

—
81:12
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْجَحِيمُ سُعِّرَتْ﴿١٢﴾

Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

—
81:13
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَإِذَا ٱلْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ﴿١٣﴾

Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

—
81:14
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّآ أَحْضَرَتْ﴿١٤﴾

Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

—
81:15
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

فَلَآ أُقْسِمُ بِٱلْخُنَّسِ﴿١٥﴾

To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

—
81:16
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

ٱلْجَوَارِ ٱلْكُنَّسِ﴿١٦﴾

Mãsu gudu suna ɓũya.

—
81:17
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَٱلَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ﴿١٧﴾

Da dare idan ya bãyar da bãya.

—
81:18
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَٱلصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ﴿١٨﴾

Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

—
81:19
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ﴿١٩﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

—
81:20
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

ذِى قُوَّةٍ عِندَ ذِى ٱلْعَرْشِ مَكِينٍ﴿٢٠﴾

Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

—
81:21
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ﴿٢١﴾

Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

—
81:22
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ﴿٢٢﴾

Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

—
81:23
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَلَقَدْ رَءَاهُ بِٱلْأُفُقِ ٱلْمُبِينِ﴿٢٣﴾

Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

—
81:24
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَمَا هُوَ عَلَى ٱلْغَيْبِ بِضَنِينٍ﴿٢٤﴾

Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

—
81:25
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَـٰنٍ رَّجِيمٍ﴿٢٥﴾

Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

—
81:26
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ﴿٢٦﴾

Shin, a inã zã ku tafi?

—
81:27
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَـٰلَمِينَ﴿٢٧﴾

Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

—
81:28
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

لِمَن شَآءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ﴿٢٨﴾

Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

—
81:29
Juz'i 30 · Hizbi 59 · Shafi 586

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿٢٩﴾

Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.

—
Aya Da Ta GabataAbasaAya Mai ZuwaAl-Infitar