Je zuwa Abubuwan Ciki
NurVerse
Al-Kur'ani Mai TsarkiLokacin SallahKalandaHadisiAddu'o'i
Ad
Ad
Ad
Ad
NurVerse

Karanta Al-Kur'ani, bi lokacin sallah, yi addu'a, ka inganta rayuwarka ta Musulunci.

© 2026 NurVerse. Duk haƙƙoƙi an kiyaye.

Saka Aikace-aikaceTuntuɓaManufar SirriSharuɗɗan Amfani
Jerin Surori
Duba Mushafu
0/52

الحاقة

Al-Haqqah

Hâkka

Makkiyya·Ayoyi 52

بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَـٰنِ ٱلرَّحِيمِ

69:1
Juz'i 29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

ٱلْحَآقَّةُ﴿١﴾

Kiran gaskiya!

—
69:2
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

مَا ٱلْحَآقَّةُ﴿٢﴾

Mẽne ne kiran gaskiya?

—
69:3
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

وَمَآ أَدْرَىٰكَ مَا ٱلْحَآقَّةُ﴿٣﴾

Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?

—
69:4
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

كَذَّبَتْ ثَمُودُ وَعَادٌۢ بِٱلْقَارِعَةِ﴿٤﴾

Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!

—
69:5
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهْلِكُوا۟ بِٱلطَّاغِيَةِ﴿٥﴾

To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.

—
69:6
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

وَأَمَّا عَادٌ فَأُهْلِكُوا۟ بِرِيحٍ صَرْصَرٍ عَاتِيَةٍ﴿٦﴾

Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.

—
69:7
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

سَخَّرَهَا عَلَيْهِمْ سَبْعَ لَيَالٍ وَثَمَـٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومًا فَتَرَى ٱلْقَوْمَ فِيهَا صَرْعَىٰ كَأَنَّهُمْ أَعْجَازُ نَخْلٍ خَاوِيَةٍ﴿٧﴾

(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.

—
69:8
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 566

فَهَلْ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٍ﴿٨﴾

To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

—
69:9
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَجَآءَ فِرْعَوْنُ وَمَن قَبْلَهُۥ وَٱلْمُؤْتَفِكَـٰتُ بِٱلْخَاطِئَةِ﴿٩﴾

Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.

—
69:10
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَعَصَوْا۟ رَسُولَ رَبِّهِمْ فَأَخَذَهُمْ أَخْذَةً رَّابِيَةً﴿١٠﴾

Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).

—
69:11
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلْمَآءُ حَمَلْنَـٰكُمْ فِى ٱلْجَارِيَةِ﴿١١﴾

Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.

—
69:12
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

لِنَجْعَلَهَا لَكُمْ تَذْكِرَةً وَتَعِيَهَآ أُذُنٌ وَٰعِيَةٌ﴿١٢﴾

Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).

—
69:13
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَإِذَا نُفِخَ فِى ٱلصُّورِ نَفْخَةٌ وَٰحِدَةٌ﴿١٣﴾

To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.

—
69:14
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَحُمِلَتِ ٱلْأَرْضُ وَٱلْجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةً وَٰحِدَةً﴿١٤﴾

Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.

—
69:15
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَيَوْمَئِذٍ وَقَعَتِ ٱلْوَاقِعَةُ﴿١٥﴾

A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.

—
69:16
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِىَ يَوْمَئِذٍ وَاهِيَةٌ﴿١٦﴾

Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.

—
69:17
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَٱلْمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرْجَآئِهَا ۚ وَيَحْمِلُ عَرْشَ رَبِّكَ فَوْقَهُمْ يَوْمَئِذٍ ثَمَـٰنِيَةٌ﴿١٧﴾

Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.

—
69:18
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

يَوْمَئِذٍ تُعْرَضُونَ لَا تَخْفَىٰ مِنكُمْ خَافِيَةٌ﴿١٨﴾

A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.

—
69:19
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقْرَءُوا۟ كِتَـٰبِيَهْ﴿١٩﴾

To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."

—
69:20
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

إِنِّى ظَنَنتُ أَنِّى مُلَـٰقٍ حِسَابِيَهْ﴿٢٠﴾

"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."

—
69:21
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَهُوَ فِى عِيشَةٍ رَّاضِيَةٍ﴿٢١﴾

Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.

—
69:22
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فِى جَنَّةٍ عَالِيَةٍ﴿٢٢﴾

A cikin Aljanna maɗaukakiya.

—
69:23
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

قُطُوفُهَا دَانِيَةٌ﴿٢٣﴾

Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),

—
69:24
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

كُلُوا۟ وَٱشْرَبُوا۟ هَنِيٓـًٔۢا بِمَآ أَسْلَفْتُمْ فِى ٱلْأَيَّامِ ٱلْخَالِيَةِ﴿٢٤﴾

(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."

—
69:25
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَأَمَّا مَنْ أُوتِىَ كِتَـٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَـٰلَيْتَنِى لَمْ أُوتَ كِتَـٰبِيَهْ﴿٢٥﴾

Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"

—
69:26
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَلَمْ أَدْرِ مَا حِسَابِيَهْ﴿٢٦﴾

"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"

—
69:27
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

يَـٰلَيْتَهَا كَانَتِ ٱلْقَاضِيَةَ﴿٢٧﴾

"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!

—
69:28
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

مَآ أَغْنَىٰ عَنِّى مَالِيَهْ ۜ﴿٢٨﴾

"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"

—
69:29
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

هَلَكَ عَنِّى سُلْطَـٰنِيَهْ﴿٢٩﴾

"Ĩkona ya ɓace mini!"

—
69:30
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

خُذُوهُ فَغُلُّوهُ﴿٣٠﴾

(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."

—
69:31
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

ثُمَّ ٱلْجَحِيمَ صَلُّوهُ﴿٣١﴾

"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."

—
69:32
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

ثُمَّ فِى سِلْسِلَةٍ ذَرْعُهَا سَبْعُونَ ذِرَاعًا فَٱسْلُكُوهُ﴿٣٢﴾

"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."

—
69:33
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤْمِنُ بِٱللَّهِ ٱلْعَظِيمِ﴿٣٣﴾

"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"

—
69:34
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلْمِسْكِينِ﴿٣٤﴾

"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

—
69:35
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 567

فَلَيْسَ لَهُ ٱلْيَوْمَ هَـٰهُنَا حَمِيمٌ﴿٣٥﴾

"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."

—
69:36
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنْ غِسْلِينٍ﴿٣٦﴾

"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."

—
69:37
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

لَّا يَأْكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلْخَـٰطِـُٔونَ﴿٣٧﴾

"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."

—
69:38
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

فَلَآ أُقْسِمُ بِمَا تُبْصِرُونَ﴿٣٨﴾

To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,

—
69:39
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَمَا لَا تُبْصِرُونَ﴿٣٩﴾

Da abin da bã ku iya gani.

—
69:40
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

إِنَّهُۥ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ﴿٤٠﴾

Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.

—
69:41
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَاعِرٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تُؤْمِنُونَ﴿٤١﴾

Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.

—
69:42
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَلَا بِقَوْلِ كَاهِنٍ ۚ قَلِيلًا مَّا تَذَكَّرُونَ﴿٤٢﴾

Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.

—
69:43
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

تَنزِيلٌ مِّن رَّبِّ ٱلْعَـٰلَمِينَ﴿٤٣﴾

Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.

—
69:44
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَلَوْ تَقَوَّلَ عَلَيْنَا بَعْضَ ٱلْأَقَاوِيلِ﴿٤٤﴾

Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.

—
69:45
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

لَأَخَذْنَا مِنْهُ بِٱلْيَمِينِ﴿٤٥﴾

Dã Mun kãma shi da dãma.

—
69:46
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

ثُمَّ لَقَطَعْنَا مِنْهُ ٱلْوَتِينَ﴿٤٦﴾

sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.

—
69:47
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

فَمَا مِنكُم مِّنْ أَحَدٍ عَنْهُ حَـٰجِزِينَ﴿٤٧﴾

Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbarMu) daga gare shi.

—
69:48
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَإِنَّهُۥ لَتَذْكِرَةٌ لِّلْمُتَّقِينَ﴿٤٨﴾

Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.

—
69:49
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَإِنَّا لَنَعْلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ﴿٤٩﴾

Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.

—
69:50
Juz'i 29 · Hizbi 57 · Shafi 568

وَإِنَّهُۥ لَحَسْرَةٌ عَلَى ٱلْكَـٰفِرِينَ﴿٥٠﴾

Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.

—
Aya Da Ta GabataAl-QalamAya Mai ZuwaAl-Ma'arij